Zabura121
Listen to this chapter
0:00
0:00
Mahajjaci Ya Daga Idonsa Sama
1
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Mai Tsaro da Ba Ya Barci
3
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Kiyaye Madawwami Mai Cikakken
7
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note