Zabura 116:12-19
12
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka ’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
Settings