Zabura 107:1-6
1
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Settings