Zabura 105:1-15
1
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku ’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Settings