Zabura 103:6-13
6
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin ’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Settings