Skip to content
Zabura 103:6-18

Zabura 103:6-18

6
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin ’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da ’ya’yansu,
18
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options