Karin Magana 8:32-36
32
“Yanzu fa, ’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Settings