Skip to content
Karin Magana 8:22-31

Karin Magana 8:22-31

22
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da ’yan adam.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options