Karin Magana 9:1-6
1
Hikima ta gina gidanta; ta yi ginshiƙansa bakwai.
2
Ta shirya abincinta gauraye da ruwan inabinta; ta kuma shirya teburinta.
3
Ta aiki bayinta mata, tana kuma kira daga wurare masu tsayi na birnin.
4
“Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo nan ciki!” Tana faɗa wa marasa hankali.
5
“Ku zo, ku ci abincina da ruwan inabin da na gauraye.
6
Ku bar hanyoyinku marasa hankali za ku kuwa rayu; yi tafiya a hanyar fahimi.
Settings