Skip to content
Karin Magana 22:12-16

Karin Magana 22:12-16

12
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options