Karin Magana 14:1-11
1
Mace mai hikima kan gina gidanta, amma da hannunta wawiya takan rushe shi ƙasa.
2
Wanda tafiyarsa ta aikata gaskiya ce kan ji tsoron Ubangiji, amma wanda hanyoyinsa ba a kan gaskiya ba ne yakan rena shi.
3
Maganar wawa kan kawo sanda a bayansa, amma leɓunan masu hikima kan tsare su.
4
Inda ba shanu, wurin sa wa dabbobi abinci zai kasance ba kome, amma daga ƙarfin saniya ce yalwar girbi kan fito.
5
Mashaidi na gaskiya ba ya ruɗu, amma mashaidin ƙarya kan baza ƙarairayi.
6
Mai ba’a kan nemi hikima amma ba ya samun kome, amma sani kan zo a sawwaƙe ga mai basira.
7
Ka guji wawa, gama ba za ka sami sani a leɓunansa ba.
8
Hikima masu la’akari shi ne su yi tunani a kan hanyoyinsu, amma wautar wawaye ruɗu ne.
9
Wawaye kan yi ba’a a gyaran zunubi, amma fatan alheri yana samuwa a cikin masu aikata gaskiya.
10
Kowace zuciya ta san ɓacin ranta, kuma babu wani dabam da zai yi rabon jin daɗinsa.
11
Za a rushe gidan mugu, amma tentin mai aikata gaskiya zai haɓaka.
Settings