Skip to content
Ƙidaya 14:1-4

Ƙidaya 14:1-4

1
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da ’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options