Ƙidaya 10:11-16
11
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
12
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
13
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
14
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
Settings