Ƙidaya 1:1-16
1
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10
daga kabilar ’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
Settings