Skip to content
Mattiyu 8:1-3

Mattiyu 8:1-3

1
Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
2
Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
3
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options