Mattiyu 5:3-10
3
“Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu, gama mulkin sama nasu ne.
4
Masu albarka ne waɗanda suke makoki, gama za a yi musu ta’aziyya.
5
Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u, gama za su gāji duniya.
6
Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci, gama za a ƙosar da su.
7
Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai, gama za a nuna musu jinƙai.
8
Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya, gama za su ga Allah.
9
Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci, gama za a kira su ’ya’yan Allah.
10
Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci, gama mulkin sama nasu ne.
Settings