Skip to content
Mattiyu 3:1-6

Wa’azin Yohanna Mai Baftisma

Mattiyu 3:1-6
1
A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
2
yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
3
Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’ ”
4
Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
5
Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
6
Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options