Mattiyu 27:59-61
59
Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
60
Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
61
Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.