Skip to content
Mattiyu 2:16-18

Hirudus ya kashe jarirai

Mattiyu 2:16-18
16
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
17
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
18
“An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options