Skip to content
Mattiyu 17:15-18

Mattiyu 17:15-18

15
Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
16
Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
17
Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
18
Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options