Skip to content
Mattiyu 15:15-20

Mattiyu 15:15-20

15
Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
16
Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
17
Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
18
Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
19
Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
20
Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options