Skip to content
Markus 9:25-27

Markus 9:25-27

25
Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
26
Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
27
Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options