Markus 15:6-11
6
Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
7
Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu ’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
8
Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
9
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
10
Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
11
Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
Settings