Markus 11:4-6
4
Suka tafi, suka kuwa tarar da wani ɗan jaki a waje, a titi, daure a ƙofar gida. Suna cikin kunce shi ke nan,
5
sai waɗansu mutane da suke tsattsaye a wurin suka ce musu, “Me kuke yi da kuke kunce ɗan jakin nan?”
6
Suka amsa kamar yadda Yesu ya ce su yi. Mutanen kuwa suka ƙyale su.