Luka 5:8-11
8
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10
Yaƙub da Yohanna, ’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
Settings