Tsallake zuwa abun ciki
Luka 4:18-21

Luka 4:18-21

18
“Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar ’yanci ga ’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da ’yanci ga waɗanda aka danne.
19
In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
20
Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
21
Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options