Luka 24:28-31
28
Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
29
Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
30
Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
31
Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Settings