Skip to content
Luka 22:24-30

Luka 22:24-30

24
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options