Luka 2:28-32
28
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30
Gama idanuna sun ga cetonka,
31
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
Settings