Luka 19:32-36
32
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
33
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
34
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
35
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
36
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
Settings