Luka 11:39-41
39
Sai Ubangiji ya ce masa, “Ku Farisiyawa, kukan wanke bayan kwano da kwaf, amma a ciki kuna cike da kwaɗayi da mugunta.
40
Ku wawayen mutane! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ne kuma ya yi cikin ba?
41
Ku ba matalauta abin da yake cikin kwano, kuma kome zai zama muku da tsabta.