Luka 1:68-74
68
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki),
71
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
Settings