Haramcin Cin Kitse da Jini
22
Ubangiji ya ce wa Musa,
23
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Kada ku ci wani kitsen shanu, ko na tumaki, ko kuwa na awaki.
24
Za a iya yin wani amfani da kitsen dabbar da ta mutu mushe, ko kitsen dabbar da namun jeji su yayyaga, amma kada a kuskura a ci.
25
Duk wanda ya ci kitsen dabbar da aka miƙa ta wuta ga Ubangiji, za a fid da shi daga mutanensa.
26
Kuma duk inda kuke zama, ba za ku ci jinin wani tsuntsu ko na dabba ba.
27
Duk wanda ya ci jini, za a fid da mutumin daga mutanensa.’ ”
Settings