Skip to content
Firistoci 22:26-30

Firistoci 22:26-30

26
Ubangiji ya ce wa Musa,
27
“Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
28
Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
29
“Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
30
Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options