31
“Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
32
Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
33
da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”