Makoki 3:37-42
37
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Settings