Makoki 3:27-39
27
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga ’yan adam ba.
34
Bai yarda a tattake ’yan kurkuku a ƙasa ba,
35
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Settings