Mahukunta 3:15-18
15
Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
16
To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
17
Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
18
Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
Settings