Skip to content
Yohanna 7:40-43

Yohanna 7:40-43

40
Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
41
Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
42
Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
43
Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options