Skip to content
Yohanna 6:16-21

Yohanna 6:16-21

16
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options