Yohanna 4:27-38
27
Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
28
Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
29
“Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
30
Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
31
Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
32
Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
33
Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
34
Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
35
Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
36
Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare.
37
Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
38
Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
Settings