Yohanna 3:5-8
5
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, ba wanda zai iya ganin mulkin Allah sai an haife shi ta wurin ruwa da kuma Ruhu.
6
Jiki yakan haifi jiki, amma Ruhu yana haifi ruhu.
7
Kada ka yi mamaki da na ce, ‘Dole ne a sāke haifarku.’
8
Iska takan hura zuwa inda take so. Kai kakan ji motsinta, sai dai ba ka iya sanin inda take fitowa ko kuwa inda za ta. Haka yake ga duk wanda aka haifa ta wurin Ruhu.”
Settings