Yohanna 10:24
Ana nuna aya 24 tare da mahallin da ke kewaye.
21
Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
22
Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
23
Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
24
sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
25
Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
26
Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27
Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
Settings