27
Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
28
Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna.
29
Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
30
Da ni da Uba ɗaya ne.”