تخطَّ إلى المحتوى
Yohanna 10:23

Yohanna 10:23

Ana nuna aya 23 tare da mahallin da ke kewaye.
20
Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
21
Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
22
Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
23
Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
24
sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
25
Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
26
Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options