Yohanna 1:6-8
6
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.