Skip to content
Ayuba 9:14-21

Ayuba 9:14-21

14
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options