Ayuba 5:17-19
17
“Mai albarka ne wanda Allah yake yi masa gyara in mutumin ya yi kuskure; saboda haka kada ka guje wa horon Maɗaukaki.
18
Ko da yake yana sa ciwo, shi ne kuma yake warkar da ciwon; ciwon da ya ji maka, shi da kansa zai warkar da shi.
19
Zai cece ka daga bala’o’i guda shida; har bakwai ma ba abin da zai same ka.
Settings