Ayuba 4:7-9
7
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.