8
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?